Ƙungiyar Amnesty International mai fafutikar kare haƙƙin ɗan’adam ta ce, dole binciken da za a yi, ya zama sanadiyar hukunta waɗanda suke da hannu a kisa tare da ƙona matafiya ƴan arewa da aka yi a garin Uromi da ke jihar Edo.
Shugaban ƙungiyar a Najeriya, Isa Sanusi ne ya bayyana haka, inda, “dole hukumomin Najeriya su tabbatar an gudanar da bincike a bayyane, sannan kuma binciken ya zama silar adalci ga waɗanda aka kashe da iyalansu. Ya kamata a riƙa bayya yadda binciken ke gudana tun daga farko har zuwa lokacin yanke hukunci.”
Amnesty ta ce abin da ya faru Uromi na nuna yadda ake ƙara samun ƙungiyar ƴan sa-kai na garuruwan da suke kusa da manyan hanyoyi suke tare hanyoyin suna aikata ba daidai ba.
“Yadda aka daɗe ana irin waɗannan kashe-kashen na nuna akwai gazawar gwamnati wajen kare rayukan al’ummarta.”
Isa Sanusi ya ƙara da cewa Amnesty ta yi Allah wadai da kisan, sannan ya sake nanata kiransu ga gwamnatin Najeriya da ta ɗauki matakin da ya dace.