fidelitybank

Dole mu zakulo wanda suka babbaka dan Bijilante a Anambra – ‘Yan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta sha alwashin farautar ‘yan baranda da suka kona ofishin kungiyar ‘yan banga na jihar Anambra da ke Amichi a lokacin da wani dan sanda ke ciki.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Tochukwu Ikenga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Awka.

Ikenga, yayin da yake magana da kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Aderemi Adeoye, ya ce babu wani dutse da za a bijiro da shi a yunkurin zakulo barayin.

‘Yan bindigar sun kai hari ofishin ‘yan banga da ke Amichi, a karamar hukumar Nnewi ta Kudu, inda suka kona shi tare da kashe wani jami’in tsaro a cikin lamarin.

Ikenga ya ce: “Kwamishanan ‘yan sandan ya yabawa kungiyoyin ‘yan banga a fadin jihar bisa jajircewar da suke yi na ganin an kare ‘yan kasa tare da tabbatar da cewa ‘yan sanda za su yi duk mai yiwuwa wajen kare su.

“Ya kuma umarci rundunonin ‘yan sanda da jami’an tsaro na musamman a fadin jihar da su gaggauta amsa duk wani kiraye-kirayen ’yan banga a duk lokacin da aka kai musu hari. Mutuwarsa ba za ta zama banza ba.”

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp