Ministoci da masu rike da mukaman siyasa da ke neman mukaman zabe na shirin bayyana a gaban kwamitin tantancewa na jamâiyyar All Progressives Congress (PAC) dauke da kwafin wasikunsu na murabus da amincewa.
Wannan ci gaban ya biyo bayan umarnin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar a ranar Larabar da ta gabata, na cewa duk mambobin majalisar ministocinsa da ke da muradin siyasa su bar ofisoshinsu a ranar Litinin, 16 ga watan Mayu ko kuma kafin ranar Litinin.
Wasu daga cikin ministoci da masu rike da mukaman siyasa sun fara yin murabus daga nadin nasu bayan umarnin shugaban kasa.
Mambobin majalisar ministocin da suka yi murabus sun hada da karamin ministan ilimi Emeka Nwajiuba; Ministan harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio; Ministan Kimiyya da Fasaha, Ogbonnaya Onu; da Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi.