Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu, ya bayyana cewa, dole ne shugaban kasa ya koma Abuja bayan kammala aikinsa da wuri a birnin Nairobi na kasar Kenya.
Politics Nigeria ta rawaito cewa, Shehu ya bayyana cewa, Buhari bai fasa zuwa birnin Landan na kasar Birtaniya ba, inda ya kara da cewa, shugaban zai tafi Landan ranar Lahadi 6 ga watan Maris.
Ya ce: “A’a, bai fasa tafiyarsa zuwa Landan ba. Har yanzu shirin ya na nan. Ya gama ziyarar aikin sa ne a Kenya, kuma ya dawo da wuri. Sannan za tafi zuwa Landan ranar Lahadi ne.”
Idan za ku tuna a safiyar yau ne Buhari ya koma Abuja ba zato ba tsammani, bayan ya halarci taron Majalisar Dinkin Duniya kan muhalli a birnin Nairobi na kasar Kenya.
Wannan dai ya saba wa shirin da ke kunshe cikin wata sanarwar manema labarai da fadar shugaban kasar ta fitar a baya, inda ta bayyana cewa shugaban zai wuce birnin Landan domin duba lafiyarsa bayan shirin na Kenya.