Gwamnan jihr Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce dole ce ta sa gwamnatinsa ke yawan rabon tallafin abinci ga mabuƙatan jihar.
Cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X ya ce gwamnatinsa na rabon tallafin ne domin magance wahalhalun da mutane suka shiga sakamakon rikicin Boko Haram, amma buƙatar gwamnatinsa shi ne kawo ƙarshen matsalar baki-ɗayanta.
Zulum ya ce yayin da gwamnatinsa ke raba tallafi ga mabuƙata da mutanen da rikicin Boko Haram da ya shafe fiye da shekara 10 ya shafa, a gefe guda kuma gwamnatin ta samu gagarumar nasara a wasu fannonin da suka shafi kiwon lafiya, da ilimi da tsaro da kuma ababen more rayuwa a jihar.
Gwamnan ya ce gwamnati na rabon tallafin ne domin rage raɗaɗi ga mutanen da suka rasa sana’o’insu sakamakon ayyukan ƙungiyar Boko Haram.
Mista Zulum ya kuma jaddada buƙatar samar da wata gidauniya da za a jima ana mora har na dogon zango, maimakon moro na lokaci guda, kamar rabon tallafi.
“Ba wai muna sa mutane su riƙa dogara da tallafin ba ne, kuna ganin ƙoƙarin da muke yi wajen farfaɗo da fannin noma, mutane su fahimci cewa dole ce take sa muke wannan abu. Mukan raba tallafi ne kawai ga mutanen da rikicin ya ɗaiɗaita, kuma sannu a hankali muna samun ci gaba”, in ji shi.
Gwamnan ya kuma duba yadda aka raba tallafin kayan abinci da wanda ba na abinci ba da kudin da suka kai naira miliyan 25 ga fiye da iyalai 25,000 a Gajiram, da ke ƙaramar hukumar Nganzai