fidelitybank

Dole ce ta sa mu ke rabon abinci akai-akai – Zulum

Date:

Gwamnan jihr Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce dole ce ta sa gwamnatinsa ke yawan rabon tallafin abinci ga mabuƙatan jihar.

Cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X ya ce gwamnatinsa na rabon tallafin ne domin magance wahalhalun da mutane suka shiga sakamakon rikicin Boko Haram, amma buƙatar gwamnatinsa shi ne kawo ƙarshen matsalar baki-ɗayanta.

Zulum ya ce yayin da gwamnatinsa ke raba tallafi ga mabuƙata da mutanen da rikicin Boko Haram da ya shafe fiye da shekara 10 ya shafa, a gefe guda kuma gwamnatin ta samu gagarumar nasara a wasu fannonin da suka shafi kiwon lafiya, da ilimi da tsaro da kuma ababen more rayuwa a jihar.

Gwamnan ya ce gwamnati na rabon tallafin ne domin rage raɗaɗi ga mutanen da suka rasa sana’o’insu sakamakon ayyukan ƙungiyar Boko Haram.

Mista Zulum ya kuma jaddada buƙatar samar da wata gidauniya da za a jima ana mora har na dogon zango, maimakon moro na lokaci guda, kamar rabon tallafi.

“Ba wai muna sa mutane su riƙa dogara da tallafin ba ne, kuna ganin ƙoƙarin da muke yi wajen farfaɗo da fannin noma, mutane su fahimci cewa dole ce take sa muke wannan abu. Mukan raba tallafi ne kawai ga mutanen da rikicin ya ɗaiɗaita, kuma sannu a hankali muna samun ci gaba”, in ji shi.

Gwamnan ya kuma duba yadda aka raba tallafin kayan abinci da wanda ba na abinci ba da kudin da suka kai naira miliyan 25 ga fiye da iyalai 25,000 a Gajiram, da ke ƙaramar hukumar Nganzai

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp