fidelitybank

Dole a tashi tsaye a kan Rasha – Biden

Date:

Shugaban Amurka Joe Biden ya yi kira ga ƙasashen Majalisar Ɗinkin Duniya da cewa jazaman ne su tashi tsaye a kan abin da ya bayyana da “tsabagen takalar faɗa” daga Rasha.

A cewarsa, tabbatar da ‘yancin cin gashin kai na kowacce ƙasa da kare haƙƙin ɗan’adam jigo ne na tanade-tanaden da ke cikin daftarin Majalisar ƙasashen duniyan.

Joe Biden yana wannan jawabi ne a wani ɓangare na Babban Taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya na shekara-shekara a birnin New York.

A cikin shekara ta biyu a jere, ya ce, wannan taro ya yi duhu sakamakon inuwar wannan yaƙi, wanda Rasha ta haddasa ba tare da an takale ta ba.

“Rasha ta yi imanin cewa duniya za ta nuna gajiyawa, kuma duniya za ta bari Rasha ta zalunci Ukraine, ba da tare da sakayya ba.

Amma ina roƙonku wannan:

Idan muka bar waɗannan jiga-jigan aƙidoji na Daftarin Majalisar Ɗinki Duniya don lallaɓa mai takalar faɗa, shin wata ƙasa, wakiliyar wannan majalisa za ta samu ƙwarin gwiwar cewa tana da tabbataccen tsaro?

Idan muka bari aka yanki sashen ƙasar Ukraine, ko ‘yancin kowacce ƙasa, zai tabbata cikin tsaro?

Biden ya ce a’a.

“Hakan ce ta sa Amurka da abokan ƙawancenmu a faɗin duniya za su ci gaba da mara baya ga mutanen Ukraine masu jarumta a lokacin da suke kare ‘yancin cin gashin kai da mutuncin iyakokin ƙasarsu – da kuma ‘yancinsu.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp