Dattijon yankin kudu maso kudu, Edwin Clark ya ce bai ga dalilin da gwamnonin arewa za su nuna adawa ga ƙudurorin gyara haraji na shugaban ƙasa Bola Tinubu ba.
Clark ya ce, “ni dai na san dole a tabbatar da ƙudurin harajin,” in ji shi a tattaunawarsa da tashar Channels.
Clark, wanda shi ne jagoran ƙungiyar ci gaban yankin Neja da Delta ta Pan Niger Delta Forum (PANDEF), ya ƙara da cewa, “na yi mamaki lokacin da na ji gwamnoni 19 na arewa sun yi wani taron daban. Idan gwamnoni 36 sun yi taro, me zai sa ku sake yin wani taron daban kuma? ina ganin yawancinsu ba su fahimci abin da suke ƙoƙarin aikatawa ba. Ya kamata su daina jijji da kai da suke yi.”
Ya ƙara da cewa dole shugaban ƙasa ya sa hikima wajen shuganci domi, “wasu tsirarun mutane na ƙoƙarin mayar da ƙasar tamkar tasu.”