Bulaliyar majalisar dattawa, Orji Kalu, ya ce fitowar Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP ya sa jam’iyyar APC ta zabi dan takararta daga yankin Arewa idan har jam’iyyar ta ci gaba da rike mulki a 2023.
Kalu, a wata sanarwa da ya fitar jim kadan bayan an ayyana Abubakar a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP na ranar Asabar, musamman ya ce jam’iyyar APC ta zabi dan takararta daga yankin Arewa maso Gabas domin Abubakar dan yankin ne.
Kalu, tsohon gwamnan jihar Abia, ya takaita zabin ne ga shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, wanda ya fito daga jihar Yobe a Arewa maso gatbas.
Lawan na daya daga cikin masu neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC.
Mataimakin shugaban kasa na yanzu, Yemi Osinbajo, tsohon gwamnan Legas, Bola Tinubu, da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, na daga cikin jiga-jigan ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC.