fidelitybank

Dole ƴanjarida da jami’an tsaro su haɗa kai domin daƙile matsalar tsaro – Janar Musa

Date:

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar CG Musa, ya nanata buƙatar da ke akwai na haɗin gwiwa tsakanin sojoji da kafofin watsa labarai domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Musa ya bayyana haka ne a wani taro da ƙungiyar ƴanjarida ta ƙasar reshen jihar Kaduna ta shirya, inda ya ce ƴanjarida na da rawar da za su taka wajen wayar da kan al’umma ta hanyar watsa labarai masu muhimmanci, da ma haɗin kan ƙasa, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Janar Musa, wanda Birgediya Janar Mohammed Kanah ya wakilta, ya ce “haɗin gwiwa tsakanin sojoji da ƴanjarida na da matuƙar muhimmanci, domin aikinmu na da muhimmanci sosai wajen gina ƙasa da saita ta.

“A daidai lokacin da sojoji suke bayar da tsaro da tabbatar da tsaro, su kuma ƴanjarida su ne suke sa ido, da bin diddigi domin tabbatar ana aikin yadda ya dace. Sai dai haɗin kai tsakanin ɓangarorin biyu na fuskantar ƙalubale, ciki har da yaɗa labaran ƙarya.”

Domin magance wannan matsala, Janar Musa ya yi kira da a ƙara fahimtar juna tsakanin ɓangarorin biyu, sannan ya buƙaci a ci gaba da horar da ƴanjarida.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp