Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, AGF, kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya yi karin haske kan cewa dokokin Najeriya sun ba da kariya mafi inganci ga masu zuba jari na kasashen waje a duniya.
Malami, SAN, ya bayyana hakan ne a ranar Litinin din da ta gabata a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar manoman shinkafa ta Najeriya (RIFAN) tare da tawagar da ta kawo ziyara daga Masarautar Hukumar Kula da Hidima ta Kasa (NSPA), Alkahira, karkashin jagorancin jakadan Masar, Moustafa Awad.
Mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a ga Malami, Dr Umar Jibrilu Gwandu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja.
A cewar sanarwar, Malami ya ce, kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999 ya ba da kariya ga duk masu zuba jari, ’yan kasa da kuma baki baki daya daga duk wani nau’i na amfani.
Ya yi nuni da cewa, an ba wa ‘yan kasashen waje damar yin rajista da hada kamfanoni a karkashin dokar Kamfanoni da Allied Matters, 2020 ba tare da wata tsangwama ba.
Ministan ya jinjinawa mambobin kungiyar manoma shinkafa ta Najeriya (RIFAN) da tawagar hukumar kula da ayyukan yi wa kasa hidima ta Masar a Najeriya, kan shirin zuba jari na bunkasa samar da abinci da kuma bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu.
Malami ya bayyana cewa, a karkashin dokar bunkasa zuba jari ta Najeriya, an ba masu zuba jari damar zuba jari da kuma shiga harkokin gudanar da duk wata sana’ar da doka ta amince da ita.