fidelitybank

Dokar zaman gida: IPOB ta harbe mutane biyu da ƙona mota guda a Enugu

Date:

Rahotonni na cewa akalla mutane biyu ne aka kashe a jiya Litinin tare da kona wata motar kirar Toyota Sienna a jihar Enugu da wasu ‘yan bindiga suka ce tana aiwatar da aiki a lokacin dokar zama a gida.

An ce ‘yan bindigar sun bude wuta a kan shahararren wurin shakatawa na Holy Ghost da misalin karfe 8:00 na safe, inda suka fatattaki ‘yan kasuwa da matafiya.

Direban motar Sienna da ta kone, wanda ya tsira da ransa, ya ce, yana tsaye a ’yan mitoci kadan daga motar yana jiran fasinjoji a lokacin da ’yan bindigar suka zo cikin wata karamar motar bas.

Ya ce, yana jin su ’yan fashi da makami ne suka gudu don ceto rayuwarsa, amma da ya waiwaya sai ya ga motar tana ci.

Rahotanni sun ce, ‘yan bindigar sun bude wuta a dajin, inda suka afkawa wasu fasinjoji. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Enugu, Daniel Ndukwe, bai amsa tambayoyin da aka yi masa kan lamarin ba a lokacin da manema labarai suka tuntubi shi.

Gwamnatin jihar IMO ta zargi ‘yan adawa da daukar nauyin masu aiwatar da wannan doka a jihar. Kwamishinan Yada Labarai da Dabaru, Cif Declan Emelumba, a wata sanarwa da ya fitar jiya, ya zargi ‘yan adawa da kitsa umarnin da kungiyar ‘yan awaren Biafra (IPOB) ta fara aiwatarwa, kafin kungiyar ta soke shi.

Sanarwar ta kuma baiwa ‘yan asalin jihar da mazauna yankin tabbacin samun tsira yayin da suke gudanar da harkokinsu.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp