Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya yi watsi da rahotannin kafafen yada labarai na cewa ‘yan majalisar sun fara tattara sa hannu, domin kalubalantar kin amincewa da shugaban kasa, Muhammadu Buhari na kin amincewa da gyara dokar zabe.
Gbajabiamila ya bayyana hakan ne ga manema labarai a fadar shugaban kasa bayan wata ganawar sirri da suka yi da Buhari a fadar da ke Abuja.
Shugaban majalisar ya na tare da shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa, Gbajabiamila na cewa “Mu na hutu a yanzu. Tarin sa hannu ba abu ne da a ke yi ba lokacin da mu ke hutu, lokacin da kowa ya watse. Abin da na fada a fili, na bayyana karara a zaman mu na karshe, cewa za mu dubi matakin kin amincewar shugaban kasa da dalilansa. Kuma idan mu ka dawo, ba abin da za mu yi a gwiwa ba ne.
“Lokacin da muka dawo daga hutun mu, har yanzu akwai isasshen lokaci, za mu yanke shawara ɗaya ko wata hanya. Wace hanya za a bi, zaɓuɓɓuka suna nan. Za mu yi abin da ya dace ga al’ummar Najeriya. Kuma na bayyana karara cewa ba za mu watsar da ruwan wankan da ya ke dauke da jariri ba,” inji Gbajabiamila
“Yan Najeriya su na so kuma ‘yan Najeriya za su samu. Wataƙila mun dakata kaɗan. Amma idan mu ka dawo, dama, akalla har zuwa majalisa, kuma na tabbata majalisar dattawa ita ma, ita ce abu na farko a ajandar mu, a makon da mu ke dawowa daga hutu.
Shugaban Majalisar Dattawan, wanda ya kuma yi magana da ‘yan jarida, ya ce kudirin kasafin kudi na shekarar 2022 na N17.13tn da a ka amince da shi kwanan nan za a mika shi ga shugaban kasa nan da mako mai zuwa, domin sanya hannu.