fidelitybank

Dokar Zabe: Kanzon kurege ne kawai batun sa hannun ‘yan majallisu – Gbajabiamila

Date:

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya yi watsi da rahotannin kafafen yada labarai na cewa ‘yan majalisar sun fara tattara sa hannu, domin kalubalantar kin amincewa da shugaban kasa, Muhammadu Buhari na kin amincewa da gyara dokar zabe.

Gbajabiamila ya bayyana hakan ne ga manema labarai a fadar shugaban kasa bayan wata ganawar sirri da suka yi da Buhari a fadar da ke Abuja.

Shugaban majalisar ya na tare da shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa, Gbajabiamila na cewa “Mu na hutu a yanzu. Tarin sa hannu ba abu ne da a ke yi ba lokacin da mu ke hutu, lokacin da kowa ya watse. Abin da na fada a fili, na bayyana karara a zaman mu na karshe, cewa za mu dubi matakin kin amincewar shugaban kasa da dalilansa. Kuma idan mu ka dawo, ba abin da za mu yi a gwiwa ba ne.

“Lokacin da muka dawo daga hutun mu, har yanzu akwai isasshen lokaci, za mu yanke shawara ɗaya ko wata hanya. Wace hanya za a bi, zaɓuɓɓuka suna nan. Za mu yi abin da ya dace ga al’ummar Najeriya. Kuma na bayyana karara cewa ba za mu watsar da ruwan wankan da ya ke dauke da jariri ba,” inji Gbajabiamila

“Yan Najeriya su na so kuma ‘yan Najeriya za su samu. Wataƙila mun dakata kaɗan. Amma idan mu ka dawo, dama, akalla har zuwa majalisa, kuma na tabbata majalisar dattawa ita ma, ita ce abu na farko a ajandar mu, a makon da mu ke dawowa daga hutu.

Shugaban Majalisar Dattawan, wanda ya kuma yi magana da ‘yan jarida, ya ce kudirin kasafin kudi na shekarar 2022 na N17.13tn da a ka amince da shi kwanan nan za a mika shi ga shugaban kasa nan da mako mai zuwa, domin sanya hannu.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp