Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I Jibril, ya ce Majalisar Dattawa ta yi wa ƙudirin haraji karatu na biyu ne domin a samu damar miƙa shi ga kwamitin kuɗi domin bibiyarsa da faɗaɗa nazari a kansa.
Cikin wata hira da BBC Sanatan mai wakiltar Kano ta Arewa ya ce, majalisar ta bayar da shawarar miƙa wa kwamitin kuɗi ya duba tare da shirya jin ra’ayin jama’a, kuma hakan ba zai yiwu ba har sai an yi wa ƙudirin karatu na biyu.
”E an ji an yi jawabai, kuma mu a nan majalisa za mu iya tambayarsu, amma ‘yan Najeriya ba za su samu damar yin tambaya game da ƙudirin ba har sai an kira jin ra’ayin jama’a”.
Sanata Barau ya ce dokar haraji ba za ta tabbata ba dole sai da masu ilimin haraji, ”kan haka ne yanzu aka tura domin su je su duba, su feɗe komai sannan su yi mana bayanin abin da ya ƙunsa”.
Ƙudirin harajin – da majalisar dattawan ta yi wa karatu na biyu a makon nan – ya haifar da ce-ce-ku-ce musamman tsakanin wasu ‘yan arewacin ƙasar, da ke zargin cewar ƙudirin zai cutar da yankin.
To amma mataimakin shugaban majalisar ya ce karatu na biyu ba shi ke nuna cewa majalisar ta amince da ƙudurin ba, ”ai a nan ne ma aikin yake farawa”.