fidelitybank

Dokar Haraji ba za ta tabbata ba dole sai da masu ilimin abun – Barau

Date:

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I Jibril, ya ce Majalisar Dattawa ta yi wa ƙudirin haraji karatu na biyu ne domin a samu damar miƙa shi ga kwamitin kuɗi domin bibiyarsa da faɗaɗa nazari a kansa.

Cikin wata hira da BBC Sanatan mai wakiltar Kano ta Arewa ya ce, majalisar ta bayar da shawarar miƙa wa kwamitin kuɗi ya duba tare da shirya jin ra’ayin jama’a, kuma hakan ba zai yiwu ba har sai an yi wa ƙudirin karatu na biyu.

”E an ji an yi jawabai, kuma mu a nan majalisa za mu iya tambayarsu, amma ‘yan Najeriya ba za su samu damar yin tambaya game da ƙudirin ba har sai an kira jin ra’ayin jama’a”.

Sanata Barau ya ce dokar haraji ba za ta tabbata ba dole sai da masu ilimin haraji, ”kan haka ne yanzu aka tura domin su je su duba, su feɗe komai sannan su yi mana bayanin abin da ya ƙunsa”.

Ƙudirin harajin – da majalisar dattawan ta yi wa karatu na biyu a makon nan – ya haifar da ce-ce-ku-ce musamman tsakanin wasu ‘yan arewacin ƙasar, da ke zargin cewar ƙudirin zai cutar da yankin.

To amma mataimakin shugaban majalisar ya ce karatu na biyu ba shi ke nuna cewa majalisar ta amince da ƙudurin ba, ”ai a nan ne ma aikin yake farawa”.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp