Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sanar da kafa dokar hana fita a faɗin jihar.
Gwamnan ya kuma umarci jami’an tsaro su tabbatar kowa ya bi wannan doka, wadda aka kafa bayan wasu ɓata-gari sun koma fasa shaguna da gine-gine yayin zanga-zangar matsin rayuwa da ke gudana a faɗin Najeriya.
Tuni dai dokar ta fara aiki nan take wanda wasu ɓata gari suka koma sace-sacen kayan gwamnati da dukiyoyin al’umma.