Hukumar kiyaye hadurra ta kasa, ta tabbatar da cewa wani hatsarin mota ya rutsa da rayukan wasu fadawan Shehun Borno guda uku, Alhaji Abubakar Umar Ibn Garbai El-kenmi, a kan hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.
Kwamandan Hukumar a jihar ta Borno, Utten Iki Boyi, ya shaida wa Jaridar Daily Trust a Maiduguri da safiyar ranar Talata cewa mutane shida ne suka yi hatsarin wanda ya afku a ranar Litinin, amma an ceto uku, inda aka kai su wani asibiti da ke kusa.
A cewarsa, lamarin ya faru ne a kusa da yankin Benisheik lokacin da motar ta yi dungure sannan ta kama da wuta.
Ya ce nan da nan suka tura jami’an su zuwa wajen da lamarin ya faru, inda aka samu mutum uku sun Æ™one kurmus har ba a iya gane su.
Sai dai ya ce an samu nasarar ceto mutum uku inda aka kai su zuwa babban asibitin Beneshiek don yi musu magani.