fidelitybank

Direbobin Tifa hudu sun shaki iskar ‘yanci a Kwara

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara, a ranar Alhamis, ta tabbatar da sakin wasu direbobi hudu da aka yi garkuwa da su ranar Laraba a wajen garin Ilorin, babban birnin jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Mista Okasanmi Ajayi ya shaidawa manema labarai a ranar Alhamis cewa, mutanen hudu da aka yi garkuwa da su sun samu ‘yanci daga wurin masu garkuwa da mutane kuma yanzu suna tare da iyalansu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ya bayyana cewa, ana ci gaba da kokarin kamo masu shirya wannan aika aika.

Ko da yake wata majiyar iyalan daya daga cikin direbobin da aka sako ta bayyana cewa an biya kudin fansa ne domin ‘yancinsu, amma rundunar ‘yan sandan ta yi shiru kan batun saboda rashin hakura da biyan kudin fansa daga iyalan wadanda aka sace.

Okasanmi, ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa ‘yan sanda bayanan da zai sa su samu nasarar aikin da suka yi.

Rahotanni sun ce, an yi wa direban tipper din kwanton bauna ne wasu mutane sanye da Uniform na sojoji suka tafi da su a wani wurin da suka je diban yashi.

Mutanen hudu da abin ya rutsa da su, an ce mambobin kungiyar masu sayar da kwalaye da yashi ne reshen garejin Oyun na Ilorin.

Masu garkuwa da mutanen, wadanda daga baya suka tuntubi iyalansu, sun bukaci kowanne iyalan da abin ya shafa a biya su Naira miliyan 5.

An ga direbobin Tifar a tsohuwar hanyar Jebba-Ilorin, dai dai da kusa da harabar kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kwara a ranar Laraba, kafin faruwar lamarin.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp