fidelitybank

Direbobin Adaidaita-sahu sun yi barazanar tafiya yajin aiki a Kano

Date:

Direbobin babur mai ƙafa uku, wanda a ka fi sani da adaidaita-sahu a Jihar Kano sun yi barazanar tsunduma yajin aiki.
Matakin na su ya biyo bayan ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana da suke yi bisa umarnin sauya lambar babur ɗin da hukumar KAROTA ta ba su.
Ko a yammacin jiya Alhamis, matuƙa baburan adaidaita+sahun sun yi cincirindo a bakin gidan tashar  Freedom Radio da ke Sharaɗa a birnin Kano domin nuna rashin goyon bayan su ga matakin.
Zanga-zangar dai ta biyo bayan yadda hukumar KAROTA ta ce sai sun biya kudi Naira 8,000 domin sabunta lambar ta su.
Sun kuma koka kan yadda KAROTA ke karɓar kuɗaɗen haraji barkatai a hannun su, musamman ma naira 100 da su ke biya kullum.
A cewar su, ba biyan naira 100 ɗin ne ke damun su ba, wacce su ke biya ta ranar lahadi, duk da cewa jami’an karɓar harajin ba sa fita aiki a ranar, amma a washegari Litinin sai a ce sai su biya har da ta ranar Lahadin.
“Kuma fa har yanzu ba a bamu na’urar nan ta ganin inda mai adaidaita-sahu ya ke ba, duk da cewa mun biya kuɗin tun sama da shekara ɗaya.
“Kullum sai an karbi kuɗaɗe a hannun mu kuma ba ma ganin amfanin kuɗin da mu ke biya,” in ji wani direban adaidaita-sahu.
Da ga ƙarshe, matuƙa baburan sun baiyana cewa da ga lokacin da hukumar KAROTA ta fara kamasu, su ma za su tafi yajin aiki.
A tuna cewa tun a farko-farkon shekarar da mu ke bankwana da ita ne matuƙa baburan adaidaita-sahu su ka tafi yajin aiki sakamakon harajin naira 100 da a ka sanya musu a kullum, inda hakan ya kawo naƙasu a kan al’amuran yau da kullum a jihar.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp