fidelitybank

Direbobi sun tayar da bore a Brazil bayan an kayar da shugaban kasa

Date:

Direbobin manyan motoci wadanda ke mara wa shugaban kasar Brazil Jair Bolsonaro baya, sun toshe tituna a fadin kasar, bayan da shugaban kasar ya sha kaye a zaben zagaye na biyu da aka gudanar a karshen mako.

Rahotonni sun ce, an rufe tituna a duka jihohin kasar in banda guda biyu, lamarin da ya haddasa cunkoso tare da shafar jigilar kayan abinci a fadin kasar.

Sakamakon zaben ya nuna cewa tsohon shugaban kasar Luiz Inácio Lula da Silva ne ya yi nasara da dan karamin rinjaye kan abokin karawarsa, kuma shugaban kasar Jair Bolsonaro.

Mista Bolsonaro dai bai kalubalanci sakamakon zaben ba, duk kuwa da cewa bai bayyana amincewa da shan kayen ba.

Akwai fargabar cewa shugaban kasar zai haifar da rudani a kasar cikin watanni biyu da suka rage kafin ya mika mulki ga sabon shugaban kasar.

Za dai a rantsar da zababben shugaban kasar ranar daya ga watan Janairun 2023.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp