Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara, a ranar Alhamis, ta tabbatar da sakin wasu direbobi hudu da aka yi garkuwa da su ranar Laraba a wajen garin Ilorin, babban birnin jihar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, Mista Okasanmi Ajayi ya shaidawa manema labarai a ranar Alhamis cewa, mutanen hudu da aka yi garkuwa da su sun samu ‘yanci daga wurin masu garkuwa da mutane kuma yanzu suna tare da iyalansu.
Kakakin rundunar ‘yan sandan ya bayyana cewa, ana ci gaba da kokarin kamo masu shirya wannan aika aika.
Ko da yake wata majiyar iyalan daya daga cikin direbobin da aka sako ta bayyana cewa an biya kudin fansa ne domin ‘yancinsu, amma rundunar ‘yan sandan ta yi shiru kan batun saboda rashin hakura da biyan kudin fansa daga iyalan wadanda aka sace.
Okasanmi, ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa ‘yan sanda bayanan da zai sa su samu nasarar aikin da suka yi.
Rahotanni sun ce, an yi wa direban tipper din kwanton bauna ne wasu mutane sanye da Uniform na sojoji suka tafi da su a wani wurin da suka je diban yashi.
Mutanen hudu da abin ya rutsa da su, an ce mambobin kungiyar masu sayar da kwalaye da yashi ne reshen garejin Oyun na Ilorin.
Masu garkuwa da mutanen, wadanda daga baya suka tuntubi iyalansu, sun bukaci kowanne iyalan da abin ya shafa a biya su N5m.
An ga direbobin tipper a tsohuwar hanyar Jebba-Ilorin, dai dai da kusa da harabar kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kwara a ranar Laraba, kafin faruwar lamarin.