Wasu mutum biyu sun mutu a wata gobarar Tankar mai da ta afku a wani gidan mai a jihar Oyo.
Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce lamarin ya faru ne a karamar hukumar Oluyole na jihar.
Sanarwar ta hukumar ta fitar yau Talata ta tabbatar da afkuwar lamarin, inda ta ce “direban Tankar da kuma yaronsa ne suka rasa ransu”.
Shugaban hukumar Yemi Akinyinka ya ce bayan samun labarin abin da ya faru ne suka aika jami’ansu don su je su kashe wutar da safiyar yau, kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito.
“Abin takaici direban tankar da kuma yaronsa sun Æ™one Æ™urmus,” in ji Akinyinka.
Bincike da aka gudanar zuwa yanzu ya nuna cewa tankar ta kwace wa direban bayan da burkinsa ya kasa aiki, abin da ya janyo ta kama da wuta.