fidelitybank

Direba ya kashe jami’an FRSC har su biyu a titin Aba

Date:

Wani direban babbar mota ya kashe jami’an Hukumar Kiyaye Aukuwar Hadura ta ƙasa har su biyu a kan babbar hanyar Aba.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar mai ɗauke da sannun babban jami’in wayar da kan jama’a na hukumar Bisi Kazeem, ya ce, muƙaddashin babban shugaban Hukumar Dauda Ali Biu, ya bayyana damuwarsa game da kashe jami’an hukumar biyu, tare da alkawarta gurfanar da waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwar jami’an a gaban kotu domin su fuskanci hukunci .

Sanarwa ta ce, Mista Biu ya yi Allah wadai da wannan lamari da ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an hukumar waɗanda ke bakin aikinsu, sakamakon abin da ya kira ‘aikin direbobi masu tukin ganganci waɗanda ke ci gaba da karya dokar tuƙi’

Lamarin ya faru ne sakamakon ƙoƙarin kauce wa rami da direban babbar motar ya yi, yayin da yake tsaka da gudu a kan hanyar, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Jami’an hukumar FRSC dai sun daɗe suna zargin direbobin ƙasar da tukin ganganci tare da gudun wuce kima a kan titunan ƙasar, lamarin da hukumar ke cewa shi ne musabbabin mafi yawancin haduran da ke aukuwa a kan titunan ƙasar.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp