Wani direban babbar mota ya kashe jami’an Hukumar Kiyaye Aukuwar Hadura ta ƙasa har su biyu a kan babbar hanyar Aba.
A wata sanarwa da hukumar ta fitar mai ɗauke da sannun babban jami’in wayar da kan jama’a na hukumar Bisi Kazeem, ya ce, muƙaddashin babban shugaban Hukumar Dauda Ali Biu, ya bayyana damuwarsa game da kashe jami’an hukumar biyu, tare da alkawarta gurfanar da waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwar jami’an a gaban kotu domin su fuskanci hukunci .
Sanarwa ta ce, Mista Biu ya yi Allah wadai da wannan lamari da ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an hukumar waɗanda ke bakin aikinsu, sakamakon abin da ya kira ‘aikin direbobi masu tukin ganganci waɗanda ke ci gaba da karya dokar tuƙi’
Lamarin ya faru ne sakamakon ƙoƙarin kauce wa rami da direban babbar motar ya yi, yayin da yake tsaka da gudu a kan hanyar, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Jami’an hukumar FRSC dai sun daɗe suna zargin direbobin ƙasar da tukin ganganci tare da gudun wuce kima a kan titunan ƙasar, lamarin da hukumar ke cewa shi ne musabbabin mafi yawancin haduran da ke aukuwa a kan titunan ƙasar.