fidelitybank

Di Maria ya yanke alakarsa da Juventus

Date:

Dan wasan tawagar Argentina, Angel Di Maria ya bar Juventus, bayan kaka daya da ya buga wa kungiyar tamaula.

Di Maria zai bar Italiya a matakin wanda yarjejeniyarsa ta kare a karshen kakar nan, wanda ake alakantashi da komawa Saudi Arabia.

Mai shekara 35, wanda ya lashe kofin duniya a Qatar tare da Argentina ya koma birnin Turin, bayan kaka bakwai da ya yi a Paris St Germain.

Di Maria ya ci wa Juventus kwallo takwas a wasa 40 da ya buga mata, kungiyar da ta kare kakar bana ba tare da daukar kofi ba.

Saudi Arabia ta ware fitattun ‘yan wasa 10 da take fatan dauka domin su koma buga gasar ta, wadanda ko dai sun lashe kofin duniya ko kuma sun dauki Champions League kamar yadda wata majiya ta sanar da AFP.

Cikin ‘yan kwallon har da Di Maria da dan wasan Real Madrid, Luka Modric da golan Tottenham, Hugo Lloris da kuma N’Golo Kante na Chelsea – dukkan ‘yan kwallon suna daf da yin ritaya.

Ranar Talata Karim Benzema ya saka hannu kan yarjejeniyar buga wa Al-Ittihad wasa, inda zai taka leda a gasar da Cristiano Ronaldo ke buga wa.

Ronaldo tsohon dan kwallon Real Madrid ya koma Al Nassr a cikin watan Janairu daga Manchester United, bayan kammala gasar kofin duniya a Qatar a 2022.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp