fidelitybank

Demokradiyya ta kasa tsinana wa matasa komai – Gbajabiamila

Date:

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya ce, dimokuradiyya ta kasa aiwatar wa matasa abun da suke so tsawon shekaru 23 da komawar ta kasar.

Gbajabiamila ya bayyana haka ne a ranar Litinin, a yayin bikin bude wani shiri na horas da matasan Najeriya na Legislative Mentorship Initiative.

Ya bayyana cewa akwai bukatar ‘yan Najeriya su zabi shugaban da zai iya tafiyar da sauye-sauye, ya kara da cewa ba zai yiwu ba a sa ran matasa su ci gaba da rike amanar dimokradiyya.

“Ba daidai ba ne a yi tsammanin matasan kasarmu za su jajirce wajen dorewar dimokuradiyyar da ba ta cimma burinsu ba,” in ji shi.

Kakakin majalisar Gbajabiamila ya jaddada cewa yawancin matasa a kasar, ba su shaida gwamnatin mulkin soja ba, don haka, ba za a yi tsammanin za su jajirce wajen tabbatar da dimokuradiyya ba tare da cin gajiyar ta ba.

Ya ce, “Najeriya na matukar bukatar shuwagabanni masu kwazo da halayya don tafiyar da canji. Sakamakon canje-canjen da ke faruwa a duniyarmu a yau zai dogara ne akan yadda muke amsawa, yanke shawara da muka yanke, da kuma ra’ayoyin da muka zaɓa don saka hannun jari a ciki. ”

Domin magance matsalar, Gbajabiamila ya ce “dole ne mu yi gaggawar daukar matakin shigar da matasa cikin harkokin siyasa da mulki. Muna yin hakan ne ta hanyar samar da hanyoyin ci gaban jagoranci”.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp