fidelitybank

Deji ya yi tir da dabi’un Melaye na tanakawa a kan lafiyar Tinubu

Date:

Shahararren dan gwagwarmayar zamantakewa da siyasa, Deji Adeyanju, ya yi Allah wadai da matakin da kakakin jam’iyyar PDP, kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, PCC, Dino Melaye, ya dauka na yin ba’a ga yanayin lafiyar dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu na jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

Melaye dai ya yi barkwanci ne game da yanayin lafiyar Tinubu ta hanyar rawan ba’a a yayin wani gangamin yakin neman zabe a jihar Delta a ranar Talata.

Da yake mayar da martani game da ci gaban, Adeyanju, a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter a safiyar Laraba, ya bayyana matakin Melaye a matsayin “mara kyau kuma ba za a yarda da shi ba”.

Ya wallafa a shafinsa na twitter cewa, “Yin ba’a ga wani saboda yanayin lafiyarsa ba shi da kyau.

“Kuna iya neman a ba da lissafi da cikakken bayyanawa daga wanda ke son zama shugaban kasa har ma da kushe su kan wannan amma ba’a a fili ba abin yarda ba ne.”

Wannan dai ba shine karo na farko da Melaye ke yiwa Tinubu ba’a ba.

A kwanakin baya ne dan siyasar haifaffen Kogi ya kalubalanci Tinubu da ya karanta Fatiha da surori uku domin ya nuna cewa shi Musulmi ne na gaskiya.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp