fidelitybank

Deji ya yi tir da dabi’un Melaye na tanakawa a kan lafiyar Tinubu

Date:

Shahararren dan gwagwarmayar zamantakewa da siyasa, Deji Adeyanju, ya yi Allah wadai da matakin da kakakin jam’iyyar PDP, kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, PCC, Dino Melaye, ya dauka na yin ba’a ga yanayin lafiyar dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu na jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

Melaye dai ya yi barkwanci ne game da yanayin lafiyar Tinubu ta hanyar rawan ba’a a yayin wani gangamin yakin neman zabe a jihar Delta a ranar Talata.

Da yake mayar da martani game da ci gaban, Adeyanju, a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter a safiyar Laraba, ya bayyana matakin Melaye a matsayin “mara kyau kuma ba za a yarda da shi ba”.

Ya wallafa a shafinsa na twitter cewa, “Yin ba’a ga wani saboda yanayin lafiyarsa ba shi da kyau.

“Kuna iya neman a ba da lissafi da cikakken bayyanawa daga wanda ke son zama shugaban kasa har ma da kushe su kan wannan amma ba’a a fili ba abin yarda ba ne.”

Wannan dai ba shine karo na farko da Melaye ke yiwa Tinubu ba’a ba.

A kwanakin baya ne dan siyasar haifaffen Kogi ya kalubalanci Tinubu da ya karanta Fatiha da surori uku domin ya nuna cewa shi Musulmi ne na gaskiya.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan Æ´ansanda mai kula da sashen kai É—auki na...

INEC za ta bai wa É—aurarru damar kaÉ—a Æ™uri’a a lokacin zaÉ“uka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ÆŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon É—an takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaÉ—i mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaÉ—i...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp