An tabbatar da cewa fitaccen mawakin Najeriya, David Adeleke da aka fi sani da Davido ko OBO zai yi wasa a bikin kammala wasannin cin Kofin Duniya a Qatar.
Mawakin mai shekara 30 shi ya jagoranci watar taken wasannin na bana da hadin-gwiwar Trinidad Cardona da Aisha, a ranar 18 ga watan Disamba za a rufe gasar.
A lokacin buÉ—e taron an shirya mawakin zai nishadantar, sai dai hakan bai samu ba sakamakon mutuwar É—an sa, Ifeanyi Adeleke.
Wannan shi ne taro na farko da Davido zai yi wasa tun bayan mutuwar É—an sa mai shekara uku, sakamakon nitse a ruwan ninkaya wato suwimin ful.