fidelitybank

David Moyes ya maye gurbin Sean Dyche a Everton

Date:

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Everton ta kammala ɗaukar David Moyes a matsayin kocin ƙungiyar a karo na biyu.

Mai shekara 61, ya sanya hannu kan kwantiragin shekara biyu da rabi a Goodison Park, bayan da ƙungiyar ta kori Sean Dyche a ranar Alhamis.

Yanzu haka Everton na matsayi na 16 a kan teburin Premier, bayan da ta yi nasara sau uku kacal a wasa 19 da ta buga a kakar bana.

Bayan sanya hannu a ƙungiyar, sabon kocin ɗan asalin Scotland ya alƙawarta mayar da Everton kan ganiyarta musamman a gasar Premier.

David Moyes ya taɓa horas da Everton daga 2002 zuwa 2013 kafin ya koma Manchester United.

Sai dai ya raba gari da United bayan wata 10 kacal, inda ya koma Real Sociedad daga bisani ya koma Sunderland sai kuma West Ham.

Kocin ya kasance ba shi da ƙungiya tun bayan barin West Ham, wadda ya ɗaukar wa kofin Europa Conference League a 2023

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp