fidelitybank

Daukewar wutar lantarki ya hana a fara zaman majalisa a kan lokaci

Date:

Wutar lantarki da aka ɗauke a zauren majalisar dokoki ta kawo jinkirin fara zaman ƴan majalisar dattijai a yau Talata.

Sanatocin sun tsaya na wani lokici yayin da suke jiran kamfanin rarraba lantarki na Abuja AEDC ya dawo da wutar.

Zauren Majlisar ya kasance cikin duhu yayin da wasu tsiraru daga cikin ƴan majalisar suke zaune suna jiran a dawo da wutar.

Sai dai daga baya shugaban majalisar, Godswill Akpabio ya buɗe zaman bayan dawowar lantarkin.

Dama dai kamfanin lantarki na AEDC ya koka kan cewa akwai ma’aikatu da hukumomin gwamnati da dama waɗanda yake bi bashi, har ma ya yi barazanar yanke musu lantarki matuƙar ba su biya bashin da ake bin su ba.

Najeriya dai na fama da ƙarancin wutar lantarki, inda ƙasar ta gaza samar da isasshen wutar lantarki da zai wadaci al’umma da masana’antu.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp