fidelitybank

Dattijo da Dansa da wani Matashi sun mutu a cikin shadda garin ciro wayar salula

Date:

Wani dattijo mai shekaru 60, Malam Danjuma, wanda aka fi sani da “Black”, da dansa, Ibrahim mai shekaru 35, da kuma Aminu Gaye, mai shekaru 35, sun mutu a cikin wani rami a bayan gida a lokacin da suke kokarin karbo wayar salula.

Saminu Abdullahi, jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi.

Ya ce hukumar ta samu kiran gaggawa daga tashar kashe gobara ta Tsanyawa da misalin karfe 11:00 na safe cewa wasu mutane hudu sun makale a cikin wani bandaki.

A cewarsa, Danjuma yana kokarin dauko wayar salula da ta fada cikin bandakin ramin, sai ya makale. Bayan haka, dansa ya shiga bandaki ramin don ya ceci mahaifinsa shi ma ya kama shi.

“Gaye da Alasan suma sun shiga ne domin ceto mutanen biyu kuma sun makale,” in ji shi.

Abdullahi ya ce an kubutar da mutum uku na farko da suka mutu a sume, yayin da na hudun kuma aka ceto da ransa.

Ya ce an mika dukkan wadanda abin ya shafa ga Sufeto Iro Lado, a sashin ‘yan sanda na Tsanyawa.

Abdullahi, ya ci gaba da cewa, rundunar ‘yan sandan ta kai wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibitin musamman na Bichi domin kula da lafiyarsu, inda likitocin da ke bakin aiki suka tabbatar da mutuwar mutane uku da kuma daya na raye.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp