fidelitybank

Dattijan Arewa sun yi Allah wadai a harin da aka kai wa Atiku a Borno

Date:

Kungiyar tuntuɓa ta dattijan arewa ta yi tir da harin da wasu `yan bangar siyasa suka kai wa kwambar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam`iyyar PDP, a Maiduguri lokacin da yake yaƙin neman zaɓe, a jiya Laraba.

Kungiyar ta yi gargadin cewa irin wannan hari na iya haddasa rikici a ƙasar matuƙar ɓangaren da aka cutar ya nemi yin ramuwar gayya.

Ta dai ja hankalin ‘yan siyasa su dinga taka wa magoya bayansu burki, idan kuma ba haka ba za ta shawarci al’umma su juya musu baya, kamar yada sakataren ƙungiyar Malam Murtala Aliyu ya shaidawa BBC.

A jiya Labara ne dai aka kai harin a lokacin da motocin Atiku ke kan hanya zuwa dandalin taro na Ramat Square da ke birnin na Maiduguri, domin yi wa magoya bayansa jawabi.

Farmakin ya yi sanadiyyar farfasa wasu motocin da ke cikin jerin gwanon, haka nan wasu bayanai na cewa akwai mutane da aka raunata.

Sai dai yan sanda a jihar Borno sun musanta cewar an kai wa ayarin motocin ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP hari.

Mai magana da yawun rundunar a jihar Borno, ASP Kamilu Shatambaya lokacin da ya gana da manema labaru, ya ce zargin kai wa ayarin motocin Atiku Abubakar hari shaci-faɗi ne kawai.

Sai dai ya ce an kama wani mutum mai suna Danladi Abbas saboda yunƙurin da ya yi na jifan ayarin motocin ɗan takaran a kan hanyar filin jirgin sama na Maiduguri.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp