fidelitybank

Dattijan Arewa sun yi Allah wadai a harin da aka kai wa Atiku a Borno

Date:

Kungiyar tuntuɓa ta dattijan arewa ta yi tir da harin da wasu `yan bangar siyasa suka kai wa kwambar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam`iyyar PDP, a Maiduguri lokacin da yake yaƙin neman zaɓe, a jiya Laraba.

Kungiyar ta yi gargadin cewa irin wannan hari na iya haddasa rikici a ƙasar matuƙar ɓangaren da aka cutar ya nemi yin ramuwar gayya.

Ta dai ja hankalin ‘yan siyasa su dinga taka wa magoya bayansu burki, idan kuma ba haka ba za ta shawarci al’umma su juya musu baya, kamar yada sakataren ƙungiyar Malam Murtala Aliyu ya shaidawa BBC.

A jiya Labara ne dai aka kai harin a lokacin da motocin Atiku ke kan hanya zuwa dandalin taro na Ramat Square da ke birnin na Maiduguri, domin yi wa magoya bayansa jawabi.

Farmakin ya yi sanadiyyar farfasa wasu motocin da ke cikin jerin gwanon, haka nan wasu bayanai na cewa akwai mutane da aka raunata.

Sai dai yan sanda a jihar Borno sun musanta cewar an kai wa ayarin motocin ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP hari.

Mai magana da yawun rundunar a jihar Borno, ASP Kamilu Shatambaya lokacin da ya gana da manema labaru, ya ce zargin kai wa ayarin motocin Atiku Abubakar hari shaci-faɗi ne kawai.

Sai dai ya ce an kama wani mutum mai suna Danladi Abbas saboda yunƙurin da ya yi na jifan ayarin motocin ɗan takaran a kan hanyar filin jirgin sama na Maiduguri.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp