fidelitybank

Dattawan Arewa sun yi titin Allah ya tsine a kan sojojin Najeriya

Date:

Kungiyar dattawan Arewa (ACF) ta yi Allah-wadai da harin da aka kai da jiragen yaƙi marasa matuka a yayin wani taron mauludi a unguwar Tudun Biri, jihar Kaduna a ranar 3 ga Disamba, 2023

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar inda ta buƙaci da a gudanar da cikakken bincike na gaskiya kan lamarin.

Ƙungiyar ta kuma bayyana lamarin a matsayin rashin ƙwarewa wajen tattara bayanan sirri.

Rundunar sojin Najeriya dai ta amince da kai harin, inda ta bayyana shi da “rashin hankali”. Rahotanni sun nunar da cewa an samu asarar rayuka, inda mutane kusan 80 galibi yara da mata ne ke fargabar sun mutu tare da jikkata wasu da dama.

Ƙungiyar ta bukaci sojoji da su fito da cikakkun bayanai don magance fargabar jama’a.

“Muna baƙatar a yi cikakken bincike, ta hanyar gaskiya da bude ido kan lamarin, don tabbatar da hakikanin abin da ya faru da wadanda ke da hannu da kuma fayyace adadin rayukan da aka rasa da kuma jikkata; Da dai sauransu. Kuma Duk wanda aka samu da laifin ko ƙwararru ko gazawar aiki dole ne a hukunta su sosai” in ji sanarwar

“Ya zama wajibi gwamnatin jihar Kaduna ta dauki matakin kare muradun wadanda abin ya shafa ba jami’an sojin Najeriya da suka aikata wannan aika-aika ba.”

“Dole ne a biya diyya ga iyalan waɗanda suka mutu daidai da darajar diyya ta Musulunci”

“Domin dawo da kwarin gwiwar jama’a, dole ne sojojin Najeriya su nemi afuwar al’ummar ƙasar da lamarin ya shafa. Bugu da kari, a matsayin alamar gaskiya, ya kamata sojojin Najeriya su gaggauta gudanar da ayyukan jinya da sauran ayyukan farfado da al’umma a cikin al’umomin da abin ya shafa.”

“Ya kamata babban hafsan tsaro ya umarci dukkan jami’an soji da su samar da ingantacciyar dabara don gujewa tabarbarewar abubuwan da suka faru a Tudun Biri, karamar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.”, sanarwar ta ƙara da cewa.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp