Kungiyar Dattawan Yammacin Afirka, ta yaba wa ‘yan Najeriya bisa jajircewarsu lokacin gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya a ranar Asabar, inda ta buƙaci ‘yan siyasa da su guji yin kalaman da za su harzuka ‘yan ƙasar.
Kungiyar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata.
Shugaban tawagar da kungiyar ta tura Najeriya domin sa-idoa zaɓe kuma tsohon shugaban ƙasar Ghana John Dramani Mahama da tsohon shugaba Goodluck Jonathan, sun buƙaci ‘yan siyasa da jam’iyyu da kuma magoya baya da su kai zuciya nesa ta hanyar samawa zaman lafiya wuri.
Kungiyar ta buƙace su da su bi hanyoyi da suka kamata wajen bin hakkokinsu.
“A don haka, muke yin kira gare su da su guji yin abubuwa da za su tayar da rikici a wannan lokaci domin kar su jefa ƙasar cikin wani yanayi na rashin zaman lafiya,” in ji Kungiyar.