Wasu ‘yan bindiga sun sace matar babban jami’in rundunar tattara bayanan sirri ta rundunar tsaro da bayar da agaji ta KASA da aka fi sani da Civil Defence, (NSCDC) a Jihar Nasarawa.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa barayin sun je gidan Mukaddashin Babban Kwamanda Apollos Dandaura a Lafia babban birnin jihar, dauke da bindigogi kirar AK-47, inda suka rika harbi domin tsorata jama’a kafin su yi gaba da matar.
Bayanai sun nuna cewa maharan sun harbi kanin kwamandan wanda shi ma jami’in rundunar ne a jihar, lokacin da suka kai harin da mislain karfe 8:30 na dare jiya Laraba.
Kakakin rundunar a jihar ta Nasarawa Mr Jerry Victor, wanda ya tabbatar wa da jaridar lamarin ya ce har yanzu ba a gano inda ‘yan bindigar suke ba.
Ya kara da cewa jami’ai sun bazama domin ceto ta ba tare da wata illa ba. Sannan ya ce zuwa yanzu barayin ba su tuntubi rundunar ko iyalin ba.