fidelitybank

Dantata ya bayar da tallafin Naira biliyan 1.5 ga ‘yan Maiduguri

Date:

Hamshakin ɗan kasuwar nan, Aminu Alhassan Dantata ya bayar da tallafin naira biliyan 1.5 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a wasu sassan Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Attajirin ɗan jihar Kano ya bayar da tallafin ne a lokacin da ya jagoranci wata tawaga daga Kano zuwa gidan gwamnatin Borno Maiduguri ranar Talata.

Ya mika ta’aziyyarsa ga Gwamna Babagana Zulum, da gwamnati da kuma al’ummar jihar baki ɗaya, musamman mutanen da suka rasa ƴan’uwansu a ambaliyar ruwa.

Dantata mai shekaru 96, ya koka kan tabarbarewar tattalin arzikin Najeriya, inda ya bukaci masu fada-a-ji da shugabannin siyasa su ji tsoron Allah a yadda suke gudanar al’amuransu.

Da yake mayar da martani, Gwamna Zulum ya nuna matukar godiya ga dattijon bisa ziyarar da ya kai masa, inda ya yi nuni da cewa hakan wata alama ce ta yadda jama’a ke tallafawa juna a lokutan tahsin hankali.

Shi ma attajiri Aliko Dangote ya bayar da tallafin naira biliyan ɗaya domin agaza wa waɗanda ambaliyar ta ɗaiɗaita.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp