fidelitybank

Dangote ya tallafawa ‘yan Sudan da suka dawo gida Najeriya

Date:

Gidauniyar Aliko Dangote ta bayar da tallafi ga wasu ‘yan Najeriya da yaƙin Sudan ya tilasta musu komawa ƙasar.

Mutane 125 da suka koma Najeriya ranar Asabar da ta gabata suka haɗar da gajiyayyu, kowannensu ya samu tallafin naira 100,000 da wasu kayyakin ihsani a cikin jaka, daga gidauniyar ta Dangote.

A cikin watan Mayu fiye da mutum 2,278 suka samu tallafin 100,000 kowannensu da abubuwan ihsani domin samun saukin haɗuwa da iyalansu, bayan dawo da su ƙasar daga Sudan.

Daga cikin mutanen da aka kwaso cikin makon da ya gabata har da wasu tsofaffi biyu da suka yi shirin zuwa Umara a mota, hanya ta bi da su ta birnin Khartoum, suka kuma faɗa tarkon yaƙin da ake gwambazawa a birnin, lamarin da ya sa suka rasa duka guzurinsu.

Wani dattijo mai suna Muhammad Saidu Ahmed ya ce ”Na dawo daga Sudan ba tare da ko sisi ba, amma yanzu na samu 100,000”.

Ita ma wata dattijuwa ta bayyana yadda ta rasa ɗanta sakamakon tashin bam a birnin Khartoum.

Matar mai shekara 80 ta ce ‘yan uwanta da dama sun tsere sakamakon hare-haren boma-bomai ba kaƙƙautawa a birnin Khartoum.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp