Dangin wata amarya a karamar hukumar Gbako ta jihar Neja sun bukaci dangin mai neman aurenta da su zo su karbi tsoffin kudi yan Naira 1000 da 500 da suka bayar a matsayin sadaki.
An tattaro cewa dangin angon sun kai wa dangin amarya wasu kudade a matsayin sadaki da sauran kayan aure yayin da ake shirye-shiryen biki.
Koda dai ba a daga daurin auren ba, iyayen yarinyar sun bayyana cewa basu shirya siyan wasu abubuwan bukata na bikin ba kuma ga shi bankin CBN ya ba da wa’adin 31 ga watan Janairu na daina karbar tsoffin kudin.
Haka kuma sun ce basu da asusun bankin da za su zuba kudin a ciki don haka suka bukaci lallai sai dai a kawo sabon kudi, rahoton Daily Trust.