Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars Ibrahim Mustapha ya lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na Najeriya na watan Fabrairu.
Mustapha ya ci kwallaye hudu a cikin watan ciki har da zura kwallaye biyu a karawar da suka yi da Sunshine Stars a filin wasa na Sani Abacha, Kano.
Dan wasan ya kara yawan kwallayen sa zuwa bakwai a NPFL sannan kuma ya kai kwallaye 60 a gasar NPFL.
Mustapha ya doke Chijoke Mbaoma da Godsgift Elkanah da Nenrot Silas da Nyima Nwagua da kuma Michael Tochukwu.
A halin da ake ciki, babban kocin Bayelsa United Meremu Okara ya lashe kyautar gwarzon koci na wata.
Okara ne ya lashe kyautar a karon farko a aikinsa na horarwa.