fidelitybank

Dan wasan Luton Town ya na son bugawa Najeriya wasa

Date:

Dan wasan gaba na Luton Town, Elijah Adebayo ya bayyana sha’awarsa ta bugawa Super Eagles ta Najeriya.

An haifi matashin mai shekaru 26 a Brent da ke Ingila ga iyayen Najeriya.

Adebayo ya cancanci ya wakilci Najeriya da Ingila a matakin kasa da kasa.

Dan wasan ya ce mahaifiyarsa za ta yi farin ciki da ganin sa ya sa rigar koriya da fari ta Najeriya.

“Ina so in buga wa Najeriya wasa,” Adebayo ya shaida wa The Times.

“Zai faranta wa mahaifiyata farin ciki, ya sa ta yi alfahari. Wannan wani abu ne da muka yi magana akai.

“Yin wasa Ingila? Zai zama lamarin duk wanda ya zo na farko. Mahaifiyata za ta yi alfahari idan na buga wa Najeriya ko Ingila wasa, amma musamman Najeriya.”

Adebayo ya ci kwallo tara a wasanni 23 da ya buga wa Luton Town a kakar bana.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp