fidelitybank

Dan uwan shugaban kasa ya kuduri niya rusa jam’iyar APC

Date:

Mamba mai wakiltar mazabar Sandamu/Daura/Maiadua a Katsina, Fatuhu Muhammad, ta yi barazanar ruguza jam’iyyar APC mai mulki a jihar sannan kuma zai koma jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), sakamakon a cewarsa “rashin adalci”, da aka yi masa a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar sa da aka kammala.

Malam Muhammad jika ga shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sha kaye a hannun Aminu Jamo. Mista Jamo ya samu kuri’u 117 yayin da Muhammadu ya samu kuri’u 30.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da a yanzu ta fara yaduwa, Mista Muhammad ya yi barazanar fice daga jam’iyyar APC.

A cikin mintuna shida da dakika ashirin da biyu da PREMIUM TIMES ta sake duba audio din, an ji dan majalisar yana fada cewa zai ruguza jam’iyyar APC a jihar Katsina.

Ya ce ba zai shiga wani sabon zabe ba idan jam’iyyar ta yanke shawarar yin daya, domin shi ne ya cancanta ya lashe zaben fidda gwani da aka gudanar a makon jiya.

“Ba za su iya yin wani zabe (na firamare) ba, saboda na ci wannan zaben yayin da suka karya doka. Sai kawai su mayar mini da tikitina, ko mu hadu a kotu ko na ruguza jam’iyyar na kawo sabuwar jam’iyya.” Inji shi.

“Ni ma zan iya zuwa in kawo jam’iyyar da ‘ya’yan itatuwa (NNPP) sai kawai su ga jam’iyyar Kwankwaso a Daura. Eh zan iya saboda kowa yana fada da kansa. Su zo su gaya wa talakawa abin da suka yi musu. Zan kuma faɗi abin da na yi wa talakawa kuma za mu ga wanda (talakawa) zai tafi,” inji shi.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp