Ƴan Najeriya sun yi wa ɗan shugaban ƙasar Bola Tinubu ca, bayan da ya buƙaci al’umma su ƙara haƙuri da mahaifinsa sanadiyyar halin da ƙasar ke ciki.
Al’umma a Najeriya na cikin ƙuncin rayuwa sanadiyyar tashin farashin kayan masarufi da taɓarɓarewar darajar kuɗin ƙasar, naira.
A wani saƙo da ya wallafa ta shafinsa na instagram, Seyi Tinubu ya ce “Ba abin jin daɗi ba ne yadda mutanen Najeriya ke shan wahala kan lamarin da ya kamata a ce an wuce batun shi tun a shekarar da ta gabata.
“Na so a ce babu waɗannan wahalhalu da ake sha.”
Ya ƙara da cewa “Sai dai wajibi ne mu jure domin jin daɗi a nan gaba.”
Bayan wanann saƙo da ya wallafa ne ƴan Najeriya da dama, musamman a shafukan sada zumunta suka mayar wa ɗan na shugaban ƙasa martani.
Shahararren mawaƙi da ake kira Charly Boy ya wallafa a shafinsa na X cewa “Seyi Tinubu na ɗaura agogon naira miliyan 350 yayin da yake ce wa ƴan Najeriya su jure wa wahalar da ake ciki, mun ji.”
Seyi na daga cikin ƴaƴan shugaba Bola Ahmed Tinubu da suka fi janyo cece-ku-ce a ƙasar.
Ko a kwanakin baya shugaban na Najeriya ya buƙaci ɗan nasa da duk wani da ba a buƙata ba da su daina shiga babban zauren taro na fadar shugaban ƙasar.