fidelitybank

Dan Tinubu ya sha caccaka bayan ya nemi a yi wa Babansa uzuri

Date:

Ƴan Najeriya sun yi wa ɗan shugaban ƙasar Bola Tinubu ca, bayan da ya buƙaci al’umma su ƙara haƙuri da mahaifinsa sanadiyyar halin da ƙasar ke ciki.

Al’umma a Najeriya na cikin ƙuncin rayuwa sanadiyyar tashin farashin kayan masarufi da taɓarɓarewar darajar kuɗin ƙasar, naira.

A wani saƙo da ya wallafa ta shafinsa na instagram, Seyi Tinubu ya ce “Ba abin jin daɗi ba ne yadda mutanen Najeriya ke shan wahala kan lamarin da ya kamata a ce an wuce batun shi tun a shekarar da ta gabata.

“Na so a ce babu waɗannan wahalhalu da ake sha.”

Ya ƙara da cewa “Sai dai wajibi ne mu jure domin jin daɗi a nan gaba.”

Bayan wanann saƙo da ya wallafa ne ƴan Najeriya da dama, musamman a shafukan sada zumunta suka mayar wa ɗan na shugaban ƙasa martani.

Shahararren mawaƙi da ake kira Charly Boy ya wallafa a shafinsa na X cewa “Seyi Tinubu na ɗaura agogon naira miliyan 350 yayin da yake ce wa ƴan Najeriya su jure wa wahalar da ake ciki, mun ji.”

Seyi na daga cikin ƴaƴan shugaba Bola Ahmed Tinubu da suka fi janyo cece-ku-ce a ƙasar.

Ko a kwanakin baya shugaban na Najeriya ya buƙaci ɗan nasa da duk wani da ba a buƙata ba da su daina shiga babban zauren taro na fadar shugaban ƙasar.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp