Mai neman jam’iyyar APC ta tsayar da shi takarar shugaban ƙasa a Najeriya, Adamu Garba, ya kaɗu da jin farashin fom ɗin takararar da jam’iyyarsu ta saka na naira miliyan 100.
A yau Laraba ne APC ta ce duk mai son ya tsaya takarar shugaban ƙasa sai ya biya kuɗin na-gani-ina-so naira miliyan 30 da kuma kuɗin fom naira miliyan 70.
Adamu Garba ya bayyana kaɗuwarsa ne a shafinsa na Twitter jim kaɗan bayan sanar da farashin.
“Miliyan 100 kuɗin fom. Lallai!,” kamar yadda ya wallafa.
Matashin da ke yawan amfani da shafukan zumunta ya kuma nemi ‘yan uwansa matasa su fito su “yaƙi jakunkunan kuɗi”.
“Ba zai yiwu mu ci gaba da sayen ofisoshin gwamnati a Najeriya ba, muna buƙatar ƙwararrun shugabanni a (zaɓen) 2023,” in ji shi.