fidelitybank

Dan takarar Sanata da da jigo a NNPP sun koma APC a Zamfara

Date:

Dan takarar Sanatan Zamfara ta Arewa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Hon. Ibrahim Son-Allah Abubakar, tare da dan takarar jam’iyyar na mazabar Zurmi da Shinkafi, Hon. Suleiman Garba Zurmi, sun koma APC.

A jawabansu daban daban, Hon. Ibrahim Dan Allah da Hon. Suleiman Garba ya ce sun koma APC ne saboda gagarumin ci gaba da aka samu wajen magance matsalar rashin tsaro a mazabunsu da gwamnatin Bello Matawalle ta yi wanda ya kawo zaman lafiya.

Sun bada tabbacin yin aiki tukuru domin samun nasarar jam’iyyar a dukkan matakai.

Da yake karbar su a APC, Gwamna Matawalle ya ce al’ummar Zamfara sun gamsu da shugabancin jam’iyyar APC a karkashin sa shi ya sa mutane da yawa ke barin jam’iyyarsu.

Ya yi alkawarin dorewar dan lokaci a yakin da yake yi da ‘yan fashi har sai an samu sakamakon da ake bukata.

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Hon Tukur Umar Danfulani ne ya mika wa gwamnan jihar ‘yan takarar jam’iyyar NNPP a fadar gwamnati dake Gusau.

Taron ya samu halartar sakataren jam’iyyar APC na jihar Zamfara, Hon.Ibrahim Umar Dangaladima; Kakakin majalisar, Hon. Nasiru Maazu Magarya; Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Kabiru Balarabe; Kwamitin aiki na jam’iyyar APC na jiha, kwamishinoni, masu ba da shawara na musamman, manyan daraktoci da magoya bayan jam’iyyar, da dai sauransu.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp