fidelitybank

Dan takarar PDP ya nuna damuwa kan barazanar tsaro a Edo

Date:

Dan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen gwamnan jihar Edo, Asue Ighodalo ya nuna damuwarsa kan barazanar tsaro a yayin da ake tsaka da kaɗa ƙuri’a a zaɓen.

Yayin da yake magana da manema labarai, Mista Ighodalo ya zargi ‘yansanda da kama ‘yan jam’iyyarsa a wata rumfar zaɓe.

“Arumfar zaɓe ta Uromi 3, wasu mutane ɗauke da makamai sun kama ɗaya daga cikin magoya bayanmu, a ƙa’ida babu wanda zai riƙe makamai a rumfar zaɓe, hakan ya sa ba wa doka, amma duk da haka sai ka ga mutane na abubuwan da ba su kamata ba, suna zaluntar jama’a tare da yunƙurin razanar da mutane,” kamar yadda ya bayyana wa manema kabarai.

Ya ƙara da cewa wannan al’amari na ɗaure masa kai, kasancewar magoya bayan jam’iyyar ne kawai ake kamawa.

”Ta yaya za a ce magoya bayan PDP ne kawai za a riƙa kamawa?, bayan ga ‘yan jam’iyyar APC nan na aikata abubuwan da ba su kamata ba, amma babu wanda ya kama su”.

Mista Ighodalo na PDP na samun gwamnan jihar Godwin Obaseki.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp