fidelitybank

Dan takarar NNPP ya tsallake rijiya da baya a Nasarawa

Date:

Tsohon kwamishinan muhalli da albarkatun kasa na Nasarawa Musa Ibrahim-Abubakar
ya tsallake rijiya da baya da ake zargin yunkurin kashe shi.

Kwanan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) zuwa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) inda ya samu tikitin tsayawa takarar dan majalisar dokokin Doma ta Kudu.

Rundunar ‘yan sandan ta fara gudanar da bincike kan lamarin, inda ta ba da tabbacin cewa za ta kama wadanda suka aikata laifin.

Jami’in hulda da jama’a, DSP Ramhan Nansel ya shaidawa manema labarai cewa an kai wa dan siyasar harin ne a hanyar Rukubi zuwa Doma.

Ibrahim-Abubakar ya ce lamarin ya faru ne a kan hanyar sa daga garin Rukubi inda ya je bayar da kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.

“Ina dawowa daga garin Rukubi zuwa Doma da misalin karfe 5:30 na yamma a kusa da kauyen Igbabo, sai wasu ‘yan bindiga kusan tara suka bude min wuta daga bangarori daban-daban.

“Daya daga cikin harsashin ya bugi wayar hannu a aljihun nono na tare da bugun gwiwar hannu da bayana”, NAN ta ruwaito yana cewa.

Ibrahim-Abubakar ya tuna cewa ya tsere zuwa kauyen Igbabo inda mutanen yankin suka taimaka suka kai shi asibiti.

Ya ce an cire harsasai da dama daga jikinsa inda likitoci ke aikin cire guda daya da ke karkashin hakarkarinsa.

Shugaban na NNPP ya kara da cewa harin na iya zama hannun abokan hamayyarsa na siyasa.

Irin wannan hari ya faru a Anambra a wannan watan. Wasu ‘yan bindiga sun yi wa ayarin motocin Sanata Ifeanyi Ubah kwanton bauna, inda suka kashe masu taimaka masa da na tsaro.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp