fidelitybank

Dan takarar NNPP ya tsallake rijiya da baya a Nasarawa

Date:

Tsohon kwamishinan muhalli da albarkatun kasa na Nasarawa Musa Ibrahim-Abubakar
ya tsallake rijiya da baya da ake zargin yunkurin kashe shi.

Kwanan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) zuwa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) inda ya samu tikitin tsayawa takarar dan majalisar dokokin Doma ta Kudu.

Rundunar ‘yan sandan ta fara gudanar da bincike kan lamarin, inda ta ba da tabbacin cewa za ta kama wadanda suka aikata laifin.

Jami’in hulda da jama’a, DSP Ramhan Nansel ya shaidawa manema labarai cewa an kai wa dan siyasar harin ne a hanyar Rukubi zuwa Doma.

Ibrahim-Abubakar ya ce lamarin ya faru ne a kan hanyar sa daga garin Rukubi inda ya je bayar da kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.

“Ina dawowa daga garin Rukubi zuwa Doma da misalin karfe 5:30 na yamma a kusa da kauyen Igbabo, sai wasu ‘yan bindiga kusan tara suka bude min wuta daga bangarori daban-daban.

“Daya daga cikin harsashin ya bugi wayar hannu a aljihun nono na tare da bugun gwiwar hannu da bayana”, NAN ta ruwaito yana cewa.

Ibrahim-Abubakar ya tuna cewa ya tsere zuwa kauyen Igbabo inda mutanen yankin suka taimaka suka kai shi asibiti.

Ya ce an cire harsasai da dama daga jikinsa inda likitoci ke aikin cire guda daya da ke karkashin hakarkarinsa.

Shugaban na NNPP ya kara da cewa harin na iya zama hannun abokan hamayyarsa na siyasa.

Irin wannan hari ya faru a Anambra a wannan watan. Wasu ‘yan bindiga sun yi wa ayarin motocin Sanata Ifeanyi Ubah kwanton bauna, inda suka kashe masu taimaka masa da na tsaro.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp