Dan takarar gwamnan jihar Legas a karkashin jam’iyyar PDP, Dr. Abdul-Azeez Olajide Adediran, wanda aka fi sani da Jandor, ya koma jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
Jandor, wanda ya yi murabus daga jam’iyyarsa ta PDP tare da kungiyar sa ta Legas4Lagos, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Ikeja, Legas.
A cewarsa, ya yanke shawarar komawa jam’iyyar APC ne saboda burinsa na bayar da gudunmawar ci gaban jihar Legas da kuma imaninsa cewa hadin kai tsakanin masu son ci gaba na da matukar muhimmanci wajen cimma muradun al’umma baki daya.
Ya bayyana cewa tafiyar da ya yi a jam’iyyar PDP a zaben gwamna na 2023 ya kasance ne bisa ga burinsa na ganin ya samu nasara a jam’iyyar da kuma yi wa al’ummar jihar Legas hidima.
Sai dai ya yi nuni da cewa yin aiki a cikin jam’iyyar APC na samar da kyakkyawan tsari na cika alkawuran da ya dauka na samar da kyakkyawan shugabanci ga daukacin al’ummar Legas.
Jandor ya kuma godewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, da kuma dan shugaban kasa, Seyi Tinubu, kan rawar da suka taka wajen ganin ya dawo jam’iyyar APC.
Tsohon dan takarar na PDP ya tabbatar wa magoya bayansa cewa ya dauki matakin ne da kyakkyawar muradun Legas, inda ya bukace su da su hada kai da shi wajen rungumar wannan sabon babi domin hada kai don gina Legas da kowa zai amfana.