fidelitybank

Dan takarar gwamnan Kano a PDP ya garzaya kotu ta kwato masa hakin sa

Date:

Rikicin da ake fama da shi kan wanene sahihin dan takarar gwamnan jihar Kano a jam’iyyar PDP har yanzu bai lafa ba.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta sanya Sadiq Wali a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar a ranar Juma’a, maimakon Muhammad Abacha, wanda ya fito a zaben fidda gwani na jam’iyyar wanda hukumar zabe ta sa ido.

Bayan faruwar lamarin, Shugaban bangaren PDP na Kano, Shehu Sagagi, ya bayyana a daren Juma’a cewa Abacha, wanda ya fusata, zai kalubalanci hukuncin INEC a kotu.

Sadiq dai dan tsohon ministan harkokin waje ne Ambasada Aminu Wali, yayin da Muhammad dan tsohon shugaban kasa ne marigayi Janar Sani Abacha.

A ranar 30 ga watan Yuni, 2022, kwamishinan zabe na jihar Kano, Farfesa Risqua Shehu, ya ce zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da ta samar da Abacha, shi ne zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP, inda ya yi nuni da cewa hukumar zabe ta lura tare da sanya ido a kan zaben.

A cewar Shehu, hukumar ta sanya ido a zaben fidda gwani na jam’iyyar, wanda ya samar da Abacha, saboda wasikar ta yi aiki a hukumance, hedkwatar jam’iyyar, bangaren Shehu Wada Sagagi ne bangaren da doka ta amince da shi, dangane da hukuncin da kotu ta yanke.

A halin da ake ciki, Sagagi ya yi ikirarin cewa, Abacha ya tabbatar masa da cewa, ya shirya yin kalubalantar jerin sunayen da INEC ta fitar da ta cire sunansa.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp