Dan takarar gwamna na jamâiyyar All Progressives Congress, APC a jihar Rivers, Tonye Cole ya goge wani sako a shafin sa na Facebook da aka tabbatar yana taya zababben shugaban kasa, Bola Tinubu murnar nasarar da ya samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar Asabar.
DAILY POST ta rawaito cewa, biyo bayan ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta kammala, Mista Cole ya wallafa sakon taya murna ga Tinubu a shafin sa na Facebook da aka tabbatar.
Sai dai wannan ya samu martani daga masu sharhi da ake kyautata zaton magoya bayan Peter Obi ne, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, LP.
Wani bincike da jaridar DAILY POST ta yi a ranar Jumaâa ya nuna cewa an goge wannan sakon ne bayan da masu raâayin rikau da ke ganin an tabka magudi a zaben shugaban kasa a jihar.
Alamu na nuna cewa Cole na iya tsammanin samun kuri’u masu yawa daga magoya bayan jam’iyyar LP wadanda suka fusata da zargin magudin zaben shugaban kasa.