Rahotanni da ke isowa daga yankin Oke Ogun a jihar Oyo na cewa daya daga cikin ‘yan takarar majalisar wakilai a jihar, Hon. Jacob Funmi Ogunmola, ya rasu.
Ogunmola, har zuwa rasuwarsa, ya kasance dan takarar majalisar wakilai a mazabar Atisbo/Saki West/Saki ta Gabas a 2023.
Ya taba zama shugaban kwamitin riko a karamar hukumar Atisbo a shiyyar Oke Ogun.
Daily Post ta tattaro cewa, Ogunmola dan asalin Ago Are ne a karamar hukumar Atisbo.
Majiyoyi sun shaida wa DAILY POST a ranar Litinin cewa Ogunmola ya rasu ne sa’o’i kadan bayan halartar wani taro a Saki ranar Lahadi.
An ce dan siyasar ya yi korafin cewa ba ya jin dadi, daga nan kuma aka garzaya da shi Legas domin kula da lafiyarsa.
An tattaro cewa Ogunmola ya rasu ne a lokacin da ake dauke shi daga Saki zuwa Legas.