fidelitybank

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Date:

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar Boko Haram Muhamad Yusuf a ƙasar Chadi mai suna Muslim Mohammed Yusuf kamar yadda kamfanin dillanci labarai na AFP ya ruwaito

An kama shi ne tare da wasu mutum biyar da ake zargin ƴan Boko Haram ne, ƙungiyar da mahaifinsa ya assasa a Najeriya a shekarun baya.

Rundunar ƴansandan Chadi ta tabbatar da kama ƴan Boko Haram shida, amma ba ta iya tantance kasancewar ɗan Muhammad Yusuf a ciki ba, kamar yadda AFP ɗin ya ruwaito.

Amma wata majiyar tsaro da kafar AFP ta zanta da su inda suka tabbatar mata da kama ƴan Boko Haram shida, ciki har da shi yaron shugaban ƙungiyar Boko Haram ɗin.

“Ƴan Boko Haram shida aka kama, kuma ɗan tsohon shugaban Boko Haram na farko ne jagoransu.”

An fi sanin Muslim da sunan Abdrahman Mahamat Abdoulaye, kuma ƙani ne ga jagoran ISWAP Habib Yusuf, wanda aka fi sani da Abu Mus’ab Al-Barnawi.

Haka kuma wani tsohon ɗan Boko Haram ya tabbatar wa AFP cewa lallai an kama Muslim a Chadi.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...

Kwallaye 6 da aka zurawa Santos a raga ta sanya Neymar ya fashe da kuka

Ɗan wasan tawagar Brazil, Neymar ya fice daga cikin...

Hukumar Shari’a ta magantu kan sadakin dubu 20 da ya yamutsa hazo a Kano

Hukumar shari’a ta jihar Kano, ta ce ba a...

Cutar Mashako ta yi ajalin Yara hudu a Kano

Rahotanni na cewa cutar mashaƙo wadda aka fi sani...

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon...
X whatsapp