fidelitybank

Dan shekara 25 ya rataye kansa a Jigawa

Date:

 

Rundunar ƴan sandan Jihar Jigawa ta ce wani matashi dan shekara 25 ya kashe kansa a karamar hukumar Taura da ke jihar.

Kakakin Rundunar Ƴan sandan Jihar, ASP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Talata a Dutse, babban birnin jihar.

Shiisu ya ce matashin ya yi amfani da wandonsa ne ya rataye kanshi a jikin wata bishiya a jiya Litinin.

Ya ce, matashin, wanda a baya aka ce ya ɓace, an same shi yana rataye a jikin bishiya a wani daji da ke wajen kauyen Zangon Maje.

“A ranar 24 ga watan Janairu da misalin karfe 2:30 na rana Hakimin Kwalam, Alhaji Muttaka Uba ya kira waya ya shaida masa cewa wani Naziru Badamasi mai shekaru 25 a kauyen Tsadawa da ke karamar hukumar Taura kuma yana fama da taɓin hankali, ya ɓata tun bayan da ya bar gida da misalin karfe 12:30 na dare.

“An same shi ne bayan ya rataye kansa da wandonsa a kan wata bishiya a wajen kauyen Zangon Maje, da ke karamar hukumar Taura,” inji shi.

Shiisu ya kara da cewa, bayan samun bayanan ne tawagar ‘yan sanda su ka je wurin da lamarin ya faru, inda suka kai gawar zuwa babban asibitin Ringim, inda wani likita ya tabbatar da mutuwar ta.

A cewarsa, daga baya an sako gawar ga ’yan uwan ​​mamacin domin a binne shi saboda babu wani zargin ko kashe shi a ka yi bayan bincike na farko.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp