fidelitybank

Dan shekara 25 ya rataye kansa a Jigawa

Date:

 

Rundunar ƴan sandan Jihar Jigawa ta ce wani matashi dan shekara 25 ya kashe kansa a karamar hukumar Taura da ke jihar.

Kakakin Rundunar Ƴan sandan Jihar, ASP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Talata a Dutse, babban birnin jihar.

Shiisu ya ce matashin ya yi amfani da wandonsa ne ya rataye kanshi a jikin wata bishiya a jiya Litinin.

Ya ce, matashin, wanda a baya aka ce ya ɓace, an same shi yana rataye a jikin bishiya a wani daji da ke wajen kauyen Zangon Maje.

“A ranar 24 ga watan Janairu da misalin karfe 2:30 na rana Hakimin Kwalam, Alhaji Muttaka Uba ya kira waya ya shaida masa cewa wani Naziru Badamasi mai shekaru 25 a kauyen Tsadawa da ke karamar hukumar Taura kuma yana fama da taɓin hankali, ya ɓata tun bayan da ya bar gida da misalin karfe 12:30 na dare.

“An same shi ne bayan ya rataye kansa da wandonsa a kan wata bishiya a wajen kauyen Zangon Maje, da ke karamar hukumar Taura,” inji shi.

Shiisu ya kara da cewa, bayan samun bayanan ne tawagar ‘yan sanda su ka je wurin da lamarin ya faru, inda suka kai gawar zuwa babban asibitin Ringim, inda wani likita ya tabbatar da mutuwar ta.

A cewarsa, daga baya an sako gawar ga ’yan uwan ​​mamacin domin a binne shi saboda babu wani zargin ko kashe shi a ka yi bayan bincike na farko.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp