Wani matashi dan shekara 17 mai suna Ojibe Chibueze ya kashe kansa bayan an zarge shi da satar kudi daga hannun ubangidansa.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Legas, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar wa manema labarai hakan a ranar Laraba.
Hundeyin ya ce wata Cynthia, wacce aka ce kanwar yaron ce ta kai karar ga ofishin ‘yan sanda na Elemoro ranar Laraba da misalin karfe 7:50 na safe.
A cewarsa, matar ta ruwaito cewa dan uwanta, Ojibe Chibueze, ya dawo daga aiki ranar Talata da misalin karfe 8:00 na dare.
Matar ta ce dan uwanta ya dauki wasu kudi ya fita, inda ta jaddada cewa daga baya ubangidansa ya kira ya sanar da ita Naira 100,000 da dan uwanta ya sace a shagonsa.
Matar ta kara da cewa dan uwanta bai dawo gida ba har sai da makwabcinta ya kira ta, wanda ya shaida mata ganin gawar dan uwan a kwance a Abijo Bus Stop, Ajah, Ibeju-Lekki, Legas.
Ta ce ta garzaya wurin da lamarin ya faru, ta tarar da gawar dan’uwanta da wani gwangwani na maharba a gefensa, wanda ta yi zaton ya sha har lahira.
“A lokacin da aka samu rahoton, nan take jami’an bincike suka je wurin da lamarin ya faru, suka tarar da gawar da kumfa na fitowa daga bakinsa da kuma hancinsa.
“An gano gwangwanin maharbi a matsayin nuni. An cire gawar kuma an ajiye ta a dakin ajiye gawa na babban asibitin Epe domin a tantance gawarwakin da kuma adana ta,” inji Hundeyin.
Ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.